فهرست کتاب‌‌ لیست کتاب‌ها

GABATARWA

da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai

tsira da aminci su kara tabbata ga fiyayyen halittu Muhammad da iyalansa tsarakaka.

 bayan haka 

Hujjoji da dalillai kan yin takiyya a muslunci daga wurin manyan Malamai guda biyu: Shaikul Ansari da Imam Ruhullahi Musawi Komaini.

Takiyya cikin kebantacciyar ma'ana ko kuma muce Takiyya da aka nakalto da wacce take cikin isdilahin harshen shari'a tsarkakakka-idan mun yi gini kan tabbatuwar samuwar hakika shar'iyya (wasu abubuwa da shari'a ce d akanta ta sanya musu suna), ko kuma kan harshen wadanda suka rayu cikin sanin bayanin shari'a daga gogaggun masana fikihu, kadai dai halascinta da hujja kanta da ingancinta na tabbata ne da dalili guda hudu daga littafin Allah da sunna da ijma'i da hankali, bari ma dai ya kusa ta wayi gari ana kidayata daga laruran addini da Mazhaba sakamakon yawan hadisai mutawatirai da suka gangaro kan bayaninta a lafazance da ma'anance da kuma a dunkule, kamar yanda bai buya ba ga dukkanin mai idanun basira ya kuma kasa kunne yana mai shaidawa, kamar misalin mas'alar yin imani da mas'alar Raja'a a wurin `yan shi'a masu daraja.

Shaikul A'azam Ansari yana cewa: asalin bayanin dalili cikin al'amarin takiyya shine wajibi ce.

Na farko: abinda Ka'idar Nafayud darar (kore cutuwa da cautarwa) kamar misalin fadinsa tsira da aminci su kara tabbata a gareshi da iyalansa tsarkaka:  

«لا ضـرر ولا ضـرار في الإسلام »

Ba cuta babu cutarwa a muslunci.

Kamar yanda ya zo cikin wasu adadin riwayoyi.1

Na biyu: hadisin dauke Alkalami cikin fadinsa (s.a.w) 

«رُفع عن اُمّتي تسعة أشياء : ومنها: (ما اضطرّوا إليه )»[2] .

 An dauke Alkalami daga barin al'umma cikin abubuwa guda tara: daga cikinsu akwai abinda suka larurantu zuwa gareshi babu yanda za su yi.

Na uku: kari kan hadisai da suke kunshe da bayani kan halascin Takiyya misalin fadinsa: 

«إنّ التقيّة واسعة ليس شيء من التقيّة إلّا وصاحبها مأجور»[3] ،

Hakika Takiyya tana da yalwa babu wani abu daga Takiyya face ma'abocin yinta na da lada.

Da wasunsu daga riwayoyi daban-daban da suka kan bayanin halascinta.

Sannan ta yiwu wani yayi wahamin cewa hakan zai lazimta cin karo da juna tsakankanin dalilan da suke bayanin halascinta da dalilan da suke bayanin wajabcin aikata aikin wajibi da haramcin aikata aikin haramun, a yayinda aka samu cin karo da juna sai muka koma zuwa ga Akbarul Ilajiya (hadisan da suka bada mafita yayin cin karo da juna) su hadisai ne da suka zo daga A'imma tsarkaka: cikin  riwayoyi guda biyu masu karo da juna, su muyi riko murajjihatul dakiliya da Karijiyya mu rinjayar inda yafi rinjaye idan da yiwuwar hakan tsakanin riwayoyin biyu amma idan su ka yi kafada da juna ta kowacce fuska babu wacce ta fifita kan daya sai ya zamana ko dai muyi watsi da dukkaninsu mu koma zuwa ga Usulul Amaliyya kamar misalin Ka'idatul Bara'a ko kuma mu zabi daya cikinsu bisa sassabawar Mabani maginai kamar yanda yake a Usulul Fikhi, kan kawar da wannan wahami ne Shaikul Ansari yayi ishara da cewa lallai su dalilan Takiyya sune suke galaba da iko cikin ma'anar isdilahi daga abinda ake kira da (Hukumatu bi ma'anar tazyiki) ko kuma fadada da'irar hukuma kansa ko kuma da ma'anar gangara (Alwurud wa nafyul maudu'il maurudi alaihi) kamar yanda yake a ilimin Usul yayin cin karo, sai yace: ( baki dayan wadannan dalilai sune suke hukunci da iko kan dalilan wajibai da haramun babu wani abu da yake cin karo daga garesu da har za a nemi mafita da kuma komawa zuwa ga Usulul Amaliyya bayan rashin samun mafita kamar yanda wasu ba'ari suka raya da wahami cikin wasu ba'arin wurare wannan mas'ala.

Sannan Shaikul Ansari a cikin Takiyya ta mustahabbi yana ganin ya kamata a tsaya a iya wacce Nassi ya zo kan halascinta baya ganin halascin tsallakawa zuwa ga abubuwan da nassin bai zo kansu, idan ma'auni da sikeli ya daidaita tsakankaninsu ya kasance daga babin Tankihul manadi da nassi ya zo kansa ko kuma idminani ba tareda samun mafita ba to lallai hakan yana daga gurbataccen kiyasi a wajenmu, wannan magana tana bukata kayi duba da lura cikinta.

Sannan yace: haka ma ababen da aka haramta da kuma halastattu da makaruhi, lallai wadannan hukunce-hukunce sun sabawa gamammun dalilai kan halascin Takiyya, saboda haka akwai bukatar kebantattun dalilai.

Takaice zance da tacewarsa cikin hukuncinta a shari'a shine cewa babu kokwanto cikin halascinta a jumlace sakamakon dalilai hudu sun tafi kan halsacinta, kan hakan akwai ijma'I da dukkanin kashe-kashensa guda biyu Almankul da Almuhassal, kari da hankali da dabi'a da suke hukunci ka zabar abu mafi sauki hatsari da ban tsoro daga mafi tsanani a yayin tsammani cutuwa, kamar yanda ayoyi da riwayoyi masu tarin suke shiryarwa da bayani kan haka.

Ta iya yiwuwa ijma'in da akai da'awa ya kasance daga ijma'i Almadaraki bawai Ta'bbudi ba wanda yake kashafi da yayewa daga maganar Ma'asumi (a.s) bari dai da ma'anar ittifakin Fakihai Malamai hakan ya kasantu ne sakamakon samun dalili daga ayoyi da riwayoyi sai ya zamana yana karfafar dalilai bawai shine dalili  da yake tsayuwa da kafafunsa ba, kari kan cewa shifa ijma'i Almuhassal yana da matukar karanci kai kace ma kwata-kwata ba samunsa kamar bai da samuwa, shi ,kuma Almankuli yana daga zato mudlaki shi kuma ba hujja bane face wanda dalili ya fitar da shi kamar misalin Kabarul Sikatu kamar yanda yake a ra'ayin Shaikul Ansari (r.a).1

Assayidul Imamul Komaini cikin wajabcin yin Takiyya da gamammun dalilai kan halascinta yana cewa:

«لا ريب في عموم أخبار التقيّة وإطلاقها كصحيحة الفضلاء، قالوا: سمعنا أباجعفر  7 يقول : التقيّة في كلّ شيء يضطرّ إليه ابن آدم فقد أحلّه اللّه له »[4] .

 (babu shakku da kokwanto cikin gamammun hadisan Takiyya da idlakinsu kamar misalin inngantattun riwayoyin marawaita masu daraj, da suka ce: mun ji Abu Jafar(a.s) yana cewa: Takiyya na cikin kowanne abu da `dan Adam ya larurantu zuwa gareshi hakika Allah ya halasta shi gareshi.4   

رواية الأعجميّ عن أبي عبد اللّه  7 في حديث أنّه قال : «لا دين لمن لاتقيّة له ». والتقيّة في كلّ شيء إلّا في النبيذ والمسح على الخفَّين .

Riwayar Ba'ajame daga Abu Abdullah (a.s) cikin wani hadisi da yake cewa: babu addini ga wanda baya Takiyya. Ita Takiyya na cikin komai face cikin giyar Nabiz da shafar Huffi biyu.

Da wasunsu dangane da mutane masu Takiyya, kashen Takiyya kan tsoro shakalai ne daban daban cikin ba'arin surori kamar tsoro kan `yan'uwa Muminai hakika gasgatuwar larura cikinsa akwai ishkali bari ma dai hani ya zo kai, gasgatuwarsa cikin koma bayan tsoro kan kansa da mabiyansa da danginsa na kusa-kusa baya nisa daga lura da zurfafawa, sai dai cewa abinda ba'arion wasu riwayoyi suke hukunci da shi shine cewa yafi gamewa da fadada daga haka, sai dai kuma anan wurin akwai magana da take bukatar runbuta da akai ishara zuwa gareshi, zahiri dai shine galibin Takiyyar A'imma ta kasance cikin fatawa ne domin kare rayukan `yan shi'arsu.

 Haka zalika babu ishkali cikin gamewarta dangane da mai ake tsoro cutuwa daga gareshi babu banbanci cikin kasancewarsa Kaifri ne ko kuma musulmi `dan Sunna ne ko waninsa, kasantuwar galibin riwayoyin da suka zo kan Takiyya suna magana kan yinta kan Ahlus-sunna sai dai cewa hakan bai kebantar da su kan iya Ahlus-sunna sakamakon rashin bayyanuwa cikin hakan duk da cewa wasu ba'arin kason hadisin sun zo iya kan Ahlus-sunna, kamar yanda zamu zo bayani kan hakan sai dai cewa zahirin galibin riwayoyin sun zo da harshen gamewa kan kowa da kowa a jumlace.

Shin halascin da ya zo cikin riwayoyin yana hadowa da wanda ake tsoro cikinsa? Zahiri shine hadda shi da kuma dalilin da ya zo kan Ka'idar kore kuntatuwa da dauke Alkalami, idan hakan ya tabbatu to wadancan dalilai za su kasance masu hukuma da iko kan dalilan da suke haramtawa da wajabta aikata wajibai, sai dai cewa magana na kasancewa ne cikin gurabe da za a iya tafiya kan togace su daga Takiyya ko kuma abinda dalili ya shiryar kansa.

Zahiri lallai Assayidul Ruhullahi Komaini (k.s) yana ganin hukuma da iko dalilan Takiyya kan dalilan wajabcin aikata wajibai da kauraccewa haramun  face abinda dalili ya togace, ya kawo ba'arin wasu gurabe da wurare da aka togace su suka fita daga Takiyya a dukkanin wuraren da aka togace ana nufin kiyaye hukunci mafi muhimmanci a mahangar shari'a, ta yiwu a wasu wuraren ya zamana an fawwala tantancewa a wuyan Mai yin takiyya don kare kansa , a wasu wuraren kuma an mika tantancewar ga mutane wandanda wurinsu aka komawa cikin ayyana ba'arin maudu'an hukunce-hukunce shari'a.

 

Assayid Ruhullahi ya bijira ya gangara kan wuraren da dalilai suka togace su daga Takiyya.6

1-daga cikinsu: wasu ba'arin abubuwan da aka haramta da ba'arin wajibai  wadanda a mahangar Mai shar'antawa da masu bayanin shari'a da suke da matukar muhimmancin misalin rusa Ka'aba da wurare masu tsarki da yanayin da zai kawar kufaifayinsu kuma ba zasu taba iya dawowa ba, hakan cikin raddui kan muslunci da Kur'ani da fassara shi da yanayin zai gurbata Mazhaba ya kuma dace da mulhidanci da makamancinsu daga manya manyan ayyukan haramun, lallai tafiya kan hukuma da iko Ka'idar nafyul haraji (kore kuntata) ko cutuwa da wasunsu kan dalilansu da zarar taken kuntata da larura da tilastuwa da cutuwa da takiyya ya tabbatu ya gasgatu tareda nesantuw ada zaukin shari'a da hadafinta, shin kai kana ganin ya dace ga musulmi yayinda aka bijira kansa da ya rushe Ka'aba dakin Allah mai Alfarma da Kabarin Manzon Allah (s.a.w) ko kuma a daure shi wata guda ko watanni biyu shin ya halasta ya rushes u domin tseratar da kansa bisa riko da hadisun Nafyul haraji kore kuntata da cutuwa? zahiri dai shine cikin misalin wandannan wurare masu daraja masu girma kai tsaye a koma zuwa Ka'idojin tazahum ba tareda karkata zuwa ga hukumar wadancan dalilai kan dalilan takiyya ba.

Da wannan ne Assayidul Ruhullahi Komaini ya nufi fitar da harshen dalilan daga cin karo da juna, ya sanya su karkashin mas'alar tazahum cikin mukamin imtisal. Sannan yace: kari kan bayyanuwarsa hadisin muwassakatu Mas'adatu yana yi masa shaida   

موثقة مسعدة بن صدقة عن أبي عبد اللّه  7 في حديث : وتفسير ما يتقى مثل أن يكون قوم سوء ظاهر حكمهم وفعلهم على غير حكم الحقّ وفعله فكلّ شيءٍ يعمل المؤمن بينهم لمكان التقيّة ممّا لا يؤدّي إلى الفساد في الدين فإنّه جائز.

Daga Mas'adatu Ibn Sadakati daga Abu Abdullah (a.s) cikin wani hadisi: tafsirin abinda ake tsoro ake takiyya kansa misalin miyagun mutane ya kasance zahirin hukuncinsu da aikinsu ya sabawa gaskiya a wannan hali duk abinda Mumini yake aikatawa tsakankaninsu ya halasta matukar dai kai haddin da zai haifar da barn aba cikin addini.

Wannan kenan tareda cewa cikin dalilin kore cutuwa akwai magana da muka yi ta cikin Risalar (La darar wa La dirar) mun yi bayanin kasancewarsa bare daga hukuma kan dalilan hukunce-hukunce.

Sannan Assayidul Komaini ya kawo wani misdaki daban cikin gabatar da hukunce-hukunce na farko kan dalilan takiyya, ko kuma muce rashin hukumar dalilan takiyya kansu, sai yace: daga wannan babi ne idan Mai takiyya ya kasance daga wanda matsayi da muhimmanci da girma a idon shari'a kamar misalin Malaman addini ta yanda aikata ba'arin wasu ayyukan haramun saboda Takiyya ko kuma barin wasu wajibai daga abinda ake kirga shi yana raunana addini d aketa alfarmarsa kamar misali ace an tilasta masa shan giya ko aikata Zina alal misali, lallai halascin Takiyya cikin misalin irin wannan mutumi da hujja riko da iko da fifituwar dalilin `dage Alkalami da na Takiyya lallai fa akwai babbar matsala bari ma dai yin hakan ya hanu bai halasta ba, ta iya yiwuwa kan wannan ne aka dora fadinsa cikin ingantacciyar riwayar Zurara da zata zo nan gaba da ake haramta yin Takiyya ga babban mutum cikin misalin shan giya- lallai Assayidul Komaini cikin wannan waiwaye da tambihi ya buga mafi kyawun misali cikin bayanin nauyin mas'uliya da aka dora ta kan wuyan Malamai da jagororin addini da cewa cikin wannan misali dole su fifita zabar shahada da mutuwa maimakon yin Takiyya don kare rayukansu sai a lura.

Sannan yace: abin da ya fi dacewa daga dukkanin wadannan abubuwa cikin rashin halascin yin Takiyya shine idan ta kasance cikin daya daga Asali daga Asalan addini ko Mazhaba ko kuma daga laruran addini suna fuskantar barazanar rugujewa da rushewa ko kuma jirkita su kamar misali ace Dawagitai da Karkatattu su yunkura canja hukuncin gado da saki da salla da hajji da wasunsu daga Asalan hukunce-hukunce ballantana Asalan Akidu da muslunci da Mazhaba, lallai Takiyya a cikin misalin wannan hali da yanayi bata halasta, sakamakon cewa dama a can ai an halasta ne donin wanzuwar Mazhaba da kare Asalai da hada kawukan musulmai kamar yanda yake cikin Takiyyar da ake yi domin kare addi da tsayar da shi da Asalansa, idan lamari ya kai ga addinin zai rushe da Asalansa a wannan lokaci Takiyya bata halasta.

Na biyu: daga wuraren aka yi togaciya- akwai shafa kan Huffi biyu da mutu'ar hajji da shan maye da giyan Nabiz da bayyana bismilla lallai abin zahirin ba'arin wasu riwayoyi yake hukunci da shi shine togace su daga yin Takiyya kamar misalin Sahihatu Zurara   

قال : قلت له : في مسح الخفَّين تقيّة ؟ فقال :ثلاثة لا أتّقي فيهنّ أحدآ: شرب المسكر ومسح الخفَّين ومتعة الحجّ . قال زرارة : ولم يقل الواجب عليكم أن لا تتّقوا فيهنّ أحدآ.

Yace: nace masa: cikin shafar Huffi biyu saboda Takiyya? Sai yace: abubuwa guda uku bana yin Takiyya cikinsu ga kowa: shan maye da shafa kan Huffi biyu da Mutu'ar Hajji. Zurara yace: bai ce wajibi kanku kada ku ji tsoran kowa cikinsu kada kuyi Takiyya cikinsu.

Sai kuma riwayar Abu Umar A'ajami:

أبو عمر الأعجمي عن أبي عبد اللّه في حديث : والتقيّة في كلّ شيءإلّافي النبيذ والمسح على الخفَّين وغيرهما.

Daga Abu Abdullahi cikin wani hadisi: yace: akwai Takiyya cikin komai face cikin gyar Nabiz da shafa kan Huffi biyu da wasunsu.

Akwai kuma wasu riwayoyin da suke kishiyantarsu kamar misalin riwayar Abu Wardi

قلت لأبي جعفر: إنّ    أباظبيان حدّثني أنّه رأى عليّآ  7 أراق الماء ثمّ مسح على الخفَّين ، فقال  : كذب أبو ظبيان ، أما بلغک قول علي  7 فيكم سبق الكتاب الخفين ، فقلت  : هل فيهما رخصة ؟ فقال : لا إلّا من عدوّ تتّقيه أو ثلج تخاف على رجليک .

Na cewa Abu Jafar (a.s): hakika Abu Zubyanu ya zantar da ni cew aya ga Aliyu (a.s) ya zubar da ruwa sannan ya shafi Huffi biyu, sai yace: Abu Zubyan ya sharara karya, ashe fadin Ali (a.s) bai zo maka: cikinku littafin Huffi biyu ya gabata, sai nace: shin cikin Huffi biyu akwai saukakawa? Sai yace: babu sai a lokacin Takiyya ko kuma babu ruwa sai kankara da kake tsoran amfani da danshinsu zai cutar da kafafunka.

ورواية صحيحة ابن أبي منصور قال : كنت عند أبي الحسن موسى  7 وعنده الكميت بن زيد، فقال للكميت : أنت الذي تقول : فالآن صرت إلى اُميّة فالاُمور لها مصائر، قال : قلت : ذاک واللّه ما رجعت عن إيماني وإنّي لكم لموالٍ ولعدوّكم لقال ولكنّي قلته على التقيّة . قال : أما لإن قلت ذلک إنّ التقيّة تجوزفي شرب الخمر.

Riwayar Abu Mansur yace: na kasance a wurin Abu Hassan Musa (a.s) a lokacin Kumaiti Ibn Zaidu yana zaune a wurinsa sai ya cewa Kumaitu: kai ne kake cewa: yanzu na koma ga Umayya lamurra garesu suke komawa, yace: na fada hakan amma wallahi hakan bai canja mini imanina ba lallai ni masoyinku ne kuma mai tsananin kiyayya da mai kinku sai dai cewa na fadi waccan magana saboda Takiyya, yace: amma lallai da ka fadi wandancananka lallai ita Takiyya tana halasta cikin shan barasa.

ورواية عمرو بن مروان التي كالصحيحة قال : قلت لأبي عبد اللّه : إنّ هؤلاءربّما حضرت معهم العشاء فيجيئون بالنبيذ بعد ذلک فإن لم أشربه خفت أن يقولوا فلاني فكيف أصنع : فقال : اكسره بالماء قلت : فإن أنا كسرته بالماء أشربه ؟ قال : لا. وغيرها.

Riwayar Amru Ibn Marwan wacce take matsayin misalin ingantacciya yace: na cewa Abu Abdullah: hakika wadannan mutane ta yiwu na hallari cin abincin dare tareda su sai su kawo Nabizi idan ban sha shi ba zai zamana in tsoro suce `dan Akida kaza ne, yaya zan yi? Sai yace ka sirka shi da ruwa ka karya shi, sai nace: idan na sirka shi da ruwa zan iya shansa kenan? Sai yace: a'a dama waninsa.

Zahiri aiki da wannan riwaya ya ayyanu sakamakon Mashhur sunyi aiki da ita, bari dai kari kan haka dama kauracewarsu daga barin riwayar da ta gabata saboda haka ba zata dace ba cikin kafa hujja da ita, bari dai larurar hankali na hakunci kan cewa barin sallah yafi muhimmanci daga shafa kan Huffi biyu haka bari aikin Hajji kan Hajjin Mutu'a tareda cewa duka biyun suna cikin abubuwan da aka togace daga Takiyya, tareda cewa muna yankewa da yakini da cewa ubangiji ba zai taba yanda da lamunta da sare wuyayu ba idan lamarin ya gudana tsakanin yin Takiyya cikin shafa Huffi bari ma dai har cikin shan giya da Nabizi da Mutu'atul Hajji.

Ya zama a bajiyeb wadancan riwayoyi da suke hana yin Takiyya a irin wadannan wurare ko kuma a yiwa wasu ba'arinsu tawili a sama musu fuska da tafsiri kamar alal misali ace: cikin misalinsu babu bukatar Takiyya, amma cikin misalin shafa kan Huffi za a iya shafar kafafu mikdarin wajibi da sunan wanke su ma'ana ya fara gabatar da hannunsa zuwa kan kafafun sai ya shafa su yayinda yake wankesu.

Sannan zai iya yiwuwa ace: ai shi wankewa ana gabatar da shi kan shafar Huffi saboda baya halasta a shafa yayinda aka samun kai kawo tsakanin wankewa da shafawa, amma cikin Mutu'atul Hajji sakamakon su suna yin dawafi da da sa'ayi mustahabbi (Dawaful Wida) yayin saukarsu Makka kan abinda aka hakaito  to mutum zai iya yin wadannan ayyuka na su da sunan Mutu'atul Hajji ita niyya lamarine da yake cikin zuciya boye saisayen mai aikin Mutu'atul Hajji lamari ne mai matukar sauki, amma shan Barasa giya da Nabizi shima za a iya kubuta daga gareshi ta hanyar kawo wasu uzurai wanda haram ba, sabida wannan ne ma halascin shan giya da sirka ta da ruwa ya zo cikin riwayar da ta gabata lokacin da aka rasa hanyar kubuta. Ta iya yiwuwa ace: barin Takiyya cikin shan giya ya kebantu da Imam (a.s) ne kadai kamar yanda Zurara ya fahimta ta yiwu hakan ta faru ne sakamakon kasancewarsa kamar sauran Fakihansu sannan Sarakunan wannan zamani basa bijirewa Fatawowinsu, tama iya yiwuwa sakamakon tattaruwa a wurinsu don gudun rigima da su cikin shugabancinsu saboda hakane zaka same su suna bada fatawa daga garesu kishiyar sauran Fakihai, ko dai sakamakon shaharar fatawarsu cikinta ta yanda Takiyya ba zata amfanar ba kamar yanda wannan sura da kaddarawa bata nesanta, ko kuma wani dalili koma bayan wannan daga tawiloli, kamar misalin dora riwayar kan rashin halascin yin Takiyya bi sannu-sannu bawai don sakamakon tsoro ba, lamarin na da sauki.

Sannan Assayin Komaini ya kara kawo wani wuri a daban daga wuraren da aka togace yin Takiyya daga dalilan halascinta, shine Jini, yana cewa: (babu shubha cikin rashin Takiyya cikin Jini lallai cikin hakan akwai Nassi da fatawa) ya zo cikin Sahihatu Muslim

صحيحة محمّد بن مسلم عن أبي جعفر قال : إنّما جعل التقيّة ليحقن بها الدم فإذا بلغ الدم فليس تقيّة .

Daga Muhammad Ibn Muslim daga Abu jafar ace: an halasta Takiyya domin kare jini da ita, idan ya zamana yin ta zai jawo zubar da jini to babu batun Takiyya.

Misalin wannan riwaya akwai Muwassakatu Abu Hamza

   Daga Abu Hamza Assumali munyi bayani filla-filla cikin littafin Almakasibul Muharrama lokacin da muke bahasi wilayar Ja'iri da abubuwa da suka dace da muhallin daga abinda yake komawa zua ga Fikhul Hadis, ku koma can.

Ya kara kawo wani gurbi d aaka togace daga dalilan Takiyya shine mas'alar barranta daga barin Sarkin Muminai Aliyu Ibn Abu Dalib (a.s) riwayoyi cikin mas'alar suna karo da juna ya kawo ya kuma fitar da natija kan ya halasta yin bara'a daga gareshi a halin Takiyya, yana cewa: Hadisai cikin Bara'a sun sassaba da junansu

1-daga cikinsu: akwai wacce take bayyana rashin halascin yin bara'a daga gareshi kamar misalin riwayar Ibn Maimun: 

محمّد بن ميمون عن جعفر بن محمّدعن أبيه عن جدّه قال : قال أمير المؤمنين : ستدْعَون إلى سبّي فسبّوني وتدعَون إلى البرائة منّي فمدّوا الرقاب فإنّي على الفطرة .

Muhammad Ibn Maimun daga Jafar Ibn Muhammad daga babansa daga kakansa yace: Sarkin Muminai yace: da sannu za nemi ku zageni za kuma a nemi ku barranta daga gareni, lallai ku sallama rayuwarku kada kuyi lallai ni ina kan gaskiya.

Da kuma riwayar Aliyu Ib Aliyu:

علي بن علي الخزاعي عن علي بن موسى عن أبيه عن آبائه عن علي بن أبي طالب أنّه قال : إنّـكم ستعرضون عن سبّي فإن خفتم على أنفسكم فسبّوني ، ألا وإنّكم ستعرضون على البرائة منّي فلا تفعلوا فإنّي على الفطرة.

  Aliyu Ibn Aliyu Alkuza'i daga Aliyu Ibn Musa daga babansa daga babanninsa daga Aliyu Ibn Abu Dalib yace: lallai ne ku zaku karkata ga zagina idan kuka ji tsoro kan salwantar rayukanku to ku zageni, lallai zaku gangara kan barranta daga gareni ka da ku sake ku barranta daga gareni lallai ne ni ina kan gaskiya.

Makamanciyar wannan riwaya shine abinda ya zo cikin Nahjul-Balaga{12} da kuma abind aya zo daga Kashshi cikin halin Hujuru Ibn Adi{13}

An samu daga Mufid cikin littafin Irshad yace: riwayoyin masu tarin sun kwarara daga Sarkin Muminai yace:

عن أميـر المؤمنيـن أنّه قال  : ستعرضون من بعدي على سبّي فسبّوني فمن عرض عليه البرائة منّي فليمدد عنقه فإن برء منّي فلا دنيا له ولا آخرة .

A bayana zaku gangara kan zagina ku zageni, duk wanda ya karkata kan barranta daga gareni to ya mika wuyansa a sare, lallai duk wanda yayi ganganci barranta daga gareni bashi da duniya bashi da lahira.

2-daga cikinsu: akwai abind aya bayyana daga sassauci cikinta da cikin mika wuya a a sare:

فعن العياشي عن أبي بكر الحضرمي عن أبي عبد اللّه  7 في حديث أنّه قيل له : مدّ الرقاب أحبّ إليک أم البرائة عن علي  7، فقال : الرخصة أحبّ إليّ، أما سمعت قول اللّهعزّوجلّ في عمّار: (إلّا مَنْ اُكْرِهَ وَقَلْبُهُ مُطْمَئِنٌ بِالإيمان ).

Daga Ayyashi daga Abubakar Hadrami daga Abu Abdullahi (a.s) cikin wani hadisi da yake cewa: mika wuya a sare ya fi soyuwa gareka ko barranta daga Aliyu (a.s) sai yace: sauki yafi soyuwa gareni, ashe baka ji fadin Allah Azza wa Jalla cikin Ammar ba: sai wanda aka tilasta shi halin zuciyarsa na cikin nutsuwa da imani).

Riwayar da ta ke kusa da wannan itace wata riwayar tasa daga Abdullahi Ibn Ajilani daga Abu Abdullahi hakan na kara bayyana cikin riwayar Yusuf Ibn Imran cikin lamarin Maisamu Ibn Yahaya Attamar.

3-daga cikinsu: abinda yake shiryarwa kan wajabcin barranta daga gareshi kamar misalin Muwassakatu Mas'ada Ibn Sadakati

مسعدة بن صدقة قال : قيل لأبي عبد اللّه  7: إنّ الناس يروون أنّ عليّآ  7 قال على منبر الكوفة : أيّها الناس إنّكم ستُدعَون إلى سبّي ثمّ تدعَون إلى البرائة منّي فلا تبرؤا منّي ؟ فقال  : ماأكثر ما يكذب الناس على علي  7، ثمّ قال : إنّما قال : إنّكم ستدعَون إلى سبّي فسبّوني ثمّ تدعَون إلى البرائة منّي وإنّي لعلى دين محمّد  9، ولم يقل  : ولاتبرؤا منّي . فقال له السائل : أرأيت أن أختار القتل دون البرائة ؟ فقال  : واللّه ما ذلک عليه و ما له إلّا ما مضى عليه عمّار بن ياسر حيث أكرهه أهل مكّة .

Mas'adatu Ibn Sadakati yace: an cewa Abu Abdullahi (a.s) lallai mutane suna ganin Aliyu (a.s) a kan Mimbarin Kufa yace: yaku Mutane da sannu za a kiraye ku zuwa ga zagina sannan za a kirayeku zuwa ga barranta daga gareni ka da ku sake ku barranta daga gareni, yace: me yafi yawa daga akewa mutane kan Aliyu (a.s)sannan yace: kadai dai yace: lallai za a kiraye ku zuwa ga zagina ku zageni sannan za a nemi ku barranta daga gareni lallai ni ina kan addinin Muhammad (s.a.w) bai ce kada ku barranta daga gareni ba. Sai mai tambaya yace masa: shin baka gani ni na zabi kisa koma bayan barranta daga Ali ba? Sai yace: wallahi babu haka kansa bai da komai face abinda Ammar Ib Yasir ya tafi a kansa kan abinda mutanen Makka suka tilasta shi aikatawa.

Da kuma riwayar Al'ihtijaj  

عن أمير المؤمنين  7 وفيها: وقد أذنت لكم في تفضيل أعدائنا إن ألجأک الخوف إليه .

Daga Sarkin Muminai (a.s) ya zo cikinta cewa: na baku izinin fifita Makiyanmu kanmu idan tsoro ya tilasta muku haka.

Sannan cikin bayyana bara'a da barranta idan tsoro da razana ya tilasaka har zuwa inda yake cewa lallai bayyanar da barrantarka daga barinmu lokacin Takiyya baya cutar damu baya kuma tauyemu, yace: na haneka na kara hanarka barin aiki da Takiyya wacce na umarceka da ita, yace: idan ka sake ka sabawa wasiyyata lallai cutuwarka kan `yan'uwanka da kanka yafi tsanani daga cutarwar da Nasibi Kafiri yake yi a kanmu.

Da kuma riwayar da Allama Majalisi ya rawaiato daga mawallafin Algarat yakoki daga Imam Sadik da Bakir (a.s).

Bai buya cewa dauke hannu daga gayyar wadancan riwayoyi da suke kunshi karyata abind aaka danganta shi zuwa ga Ali (a.s) daga hadisan Takiyya daga fadinsa madaukaki: 

 (وَلا تُلْقوا بِأيْديكُمْ إلى التَهْلُكَة)

Kada ku sanya hannayenku cikin halaka.

Da kuma hukuncin hankali da yake lazimta kiyaye rai da himmatiwar ubangiji da shi ba zai taba yiwuwa cikin riko da misalin wadancan riwayoyi da ba a da yakini kansu basu da yankakken isnadi ba ace mu ajiye aiki da Takiyya da kare rayuka.

Da wannan ne Assayidul Komaini ya rinjayar da gayya ta uku daga riwayoyi sakamakon riko rinjaye na cikin gida kamar misalin karfin isnadi d ayake cikinsu da kuma rinjaye na waje kamar misalin ayar da ta gabata da take hani da jefa hannu cikin halaka da himmatuwar hankali da ubangiji kan kare rai da kuma hadisan halascin aiki da Takiyya, sannan yace: da'awar da Mufid yayi ba za ta fa'idantar damu ba da yakini ba, lallai mu bamu yi tuntube da riwaya ko da guda daya ba da take kunshe da abinda Mufid ya ambata.

Na'am ba'arin ma'anarsa tana da cewa wasu raunanan riwayoyi da su ka gabata da suke kishiyantar riwayoyin da ba'arinsu suka fisu karfi kyawuntar isnadi ga kuma wadancan riwayoyi kari kan raunanarsu cike suke da zagi da la'ana da sassabawa, sannan tabbataccen al'amari ne cewa ubangiji ba zai yarda da mika wuya a sare ba kamar yanda riwayar Al'ihtijaj ta kunsa.

Sannan Assayidul Komaini ya jawo hankali zuwa ga wata nukta mai taushi cikin Kissar Maisan Tammar Allah ya kara masa yarda, duk da cewa ya saba da zahiri, yana cewa: amma lamarin Maisam duk da cewa sananniyar Kissace kuma tabbatuwar ta bai nesanta a jumlace sai dia cewa batun a hakika saninsa ya na komawa zuwa ga Imam (a.s) ta yiwu yana da sani da cewa tsinannen mutum Ubaidullahi Ibn Zayad shine zai kashe Maisam Tammar a cikin kowanne hali ko da Maisam ya barranta daga Ali (a.s) ko bai barranta ba, barrantarsa zata kasance ba zata amfana masa komai b aba zata kubutar jininsa, saboda haka shi bai halasta ya barranta daga gareshi bah aka bai ya halasta yayi zagi duka don neman kubuta tun da dai ba zai kubuta ba