فهرست کتاب‌‌ لیست کتاب‌ها
■ KALMAR TARBIYYA CIKIN HARSHEN LARABCI DA YANDA AKA YI 4
■ FASALI NA ( 2 ) 24
■ AUREN DABI'A 24
■ FASALI NA 3
■ FASALI NA 4 73
■ FASALI NA 5 131
■ FASALI NA 6 176
HAQQOQIN DA MA'AURATA SU KAYI TARAYYA CIKI 177
1 – HAQURI 178
2 – KAMEWA DAGA ZALUNCI DA CUATARWA 179
HAQQOQIN MATA 180
CIYARWA DA YALWATAWA 185
TAUSAYAWA DA KAMEWA DAGA ZALUNCI 187
KAMEWA DAGA BARIN DUKA MAI CUTARWA 187
UMARNI DA KYAKKYAWA DA HANI DA MUMMUNA 193
GARKUWA 196
8 – KYAUTATAWA : 196
9 - KYAWUNTA ZAMANTAKEWA 197
3 – TAUSAYAWA MIJI : 208
4 – HIMMATUWA DA KULA DA CIKIN GIDA DA KAYYAKINSA : 209
5 - HIMMATUWA CIKIN SAUKE HAQQOQI 209
6 – JIMA'I 210
7 - ADO 213
8 – KAMEWA CIKIN MAGANA : 219
SHUGABANTAR IYALI 225
DALILAI DA SUKE SANYA DAWWAMAR AURE 227
1 – SON JUNA 228
2 – YAWAITA AIKATA ALHERI: 228
4 – SANYA FARIN CIKI: 229
5 – BIYAYYA DA NEMAN YARDAR MIJI: 230
6 – KIYAYE MUTUNCI DA DUKIYA : 230
7 – TAIMAKO DA TALLAFAWA 230
8 – TARBAR MIJI DA KYAWUNTA BANKWANA DA SALLAMA : 231
9 – KALAMIN AQIDOJI MAI KYAWU DA QARFAFAFFEN FURUCI. 232
10 – KARBAR UZURI DA YIWA JUNA UZURI : 232
11 – BINSU SANNU SANNU CIKIN KOWANNE HALI : 233
12 – KYAWUNTA LAFAZI CIKN KOWANNE YANAYI : 233
13 – RASHIN SAURARON KYAUTATA AIKI DARI BISA DARI 233
14 – RASHIN IKON DAUKAR NAUYI A RAYUWANCE : 234
15 – RASHIN GORI KAN MIJI : 234
16 – RASHIN QAURACEWA AL'AMARIN SHIMFIDA: 235
17 - YIN SHAWARA DA MATA BANDA BIYE MUSU: 235
18 – TAKA TSAN TSAN DA KUMA FARKAWA : 238
19 – HANKALTA 239
20 - MIJI SHI NE MUTUNCIN MATARSA 240
21 – KISHI 240
22 – TAIMAKEKENIYYA 242
23 – DADADAWA IYALI 243
27 – WATSI DA BOAKANCI DA TSAFE TSAFE : 244
28 - HIDIMA MADAWWAMIYA 245
29 – GODIYA 246
29 – QAUNAR JUNA 247
TSINTUWA GUDA BIYU GIDAN ALI DA FATIMA (AS) 248
■ FASALI NA 8 252

KACIYA 287

MUQAMI NA 11

                                                          KACIYA

Daga ladubban muslunci bayan haihuwa shi ne yi ma abin da aka haifa kaciya rana ta bakwai da haihuwarsa, haka ma ana yiwa yarinya mace.

عن النبيّ (صلى الله عليه وآله)  : الختان سنّة للرجال .

1 – daga annabi (saw) : kaciya sunna ce ga `ya`ya maza.

وكتب عبد الله بن جعفر الحميري إلى أبي محمّد الحسن بن علي (عليه السلام)  : أ نّه روي عن الصالحين أن اختنوا أولادكم يوم السابع يطهروا ، فإنّ الأرض تضجّ إلى الله من بول الأغلف ، وليس ـ  جعلني الله فداك  ـ في حجّامي لدنا حَذَق بذلك ـ  أي يعرف هذه المهنة جيّداً  ـ ولا يختنونه يوم السابع وعندنا حجّام من اليهود ، فهل يجوز لليهود أن يختنوا أولاد المسلمين أم لا  ؟ قال  : فوقّع (عليه السلام)  : يوم السابع ، فلا تخالفوا السنن إن شاء الله

2 – Abdullah dan jafar alhimyari ya rubuta wasiqa zuwa ga baban muhammadu hassan dan ali (as) cewa shi ya rawaito daga salihai cewa ku yiwa yaranku kaciya rana ta bakwai da haihuwarsu, lalle qasa na kaima Allah qarar fitsarin lusari (mara kaciya ) raina fansarka ba mu da wanzamin da ya ke da  kware kan kaciya, mutane ba sa yin  kaciya rana ta bakwai, muna da wani wanzami bayahude shin ya  halasta ya yiwa yaran musulmai kaciya ko bai halasta ba? sai imam ya ce: ku yi rana ta bakwai ka da ku sabawa sunnoni da yardar Allah.

من طبّ الأئمة ، عن النبيّ (صلى الله عليه وآله) ، قال  : اختنوا أولادكم في السابع فإنّه أطهر وأسرع لنبات اللحم ، فقال  : إنّ الأرض تنجس ببول الأغلف أربعين يوماً

3 – daga littafin dibbul a'imma, annabi (saw) ya ce: ku yiwa yaranku kaciya rana ta bakwai lalle hakan ya fi sauri ga tsirowar nama, ya ce: lalle qasa na najastuwa da fitsarin lusari mara kaciya tsawon kwanaki arba'in.

عن الصادق (عليه السلام) ، قال  : ثقب اُذن الغلام من السنّة ، وختانه لسبعة أيام من السنّة ، وخفض النساء مكرمة ، وليست من السنّة ، وأيّ شيء أكرم من المكرمة

4 – sadiq (as) : huda kunnen yaro da yi masa kaciya na daga cikin sunnoni, kaciye mata ba wajibi ba ne mustahabbi ne.

ومن تهذيب الأحكام ، عن الصادق (عليه السلام) ، قال  : لمّـا هاجرت النساء إلى رسول الله (صلى الله عليه وآله) ، هاجرت فيهن امرأة يقال لها  : اُمّ حبيبة ، وكانت خافضة تخفض الجواري ، فلمّـا رآها رسول الله (صلى الله عليه وآله) قال لها  : يا اُمّ حبيبة ، العمل الذي كان في يدك هو في يدك اليوم  ؟ قالت  : نعم يا رسول الله ، إلاّ أن يكون حراماً فتنهاني عنه . قال  : لا ، بل هو حلال ، فادني منّي حتّى اُعلّمكِ ، فدنت منه فقال  : يا  اُمّ  حبيبة ، إذا أنت فعلتِ فلا تنهكي أي لا تستأصلي وأشمي ـ  النهك المبالغة في كلّ شيء ، وأشمت الخافضة البظر أي أخذت منه قليلا  ـ فإنّه أشرق للوجه وأحظى عند الزوج . قال  : فكانت لاُمّ حبيبة اُخت يقال لها  : اُمّ عطيّة ، وكانت مقيّنة ، يعني قاشطة ، فلمّـا انصرفت اُمّ حبيبة إلى اُختها أخبرتها بما قال لها رسول الله (صلى الله عليه وآله)فأقبلت اُمّ عطيّة إلى النبيّ (صلى الله عليه وآله) فأخبرته بما قالت لها اُختها ، فقال لها  : اُدني منّي يا  اُمّ عطيّة ، إذا أنتِ قيّنت الجارية ـ  أي زيّنت الجارية  ـ فلا تغسلي وجهها بالخرقة ، فإنّ الخرقة تذهب بماء الوجه

5 – daga tahzibul ahkam, daga imam sadiq (as) ya ce: lokacin da mata suka yi hijira zuwa ga manzon Allah (saw) wata mata da ake kira ummu habiba ta kasance cikinsu ta kasance tana yima mata kaciya, yayain da manzon Allah (as) sai ya ce mata: ya ummu habiba aikin nan da ya kasance a hannunki har ya zuwa yau dinnan ya na hannunki? sai tace: na'am ya manzon Allah (saw) sai dai idan ya kasance haramun sai ka hane ni  ga barinsa, sai ya ce : a'a halali ne, matso kusa dani in koyar da ke, sai matsa kusa da shi, sai ya ce: ya ummu habiba idan za kiyi ka da ki gutsire gaba daya ki dan yanki kadan – lalle hakan ya fi haskaka ga fuska da dadi ga miji, ummu habiba ta na da wata `yar'uwa da ake kira da ummu adiyya ta kasance mai yiwa mata kwalliya, yayin da ummu habiba ta je wajen `yar'uwarta ummu adiyya sai ta bata labarin abin da  manzon Allah (saw) ya gaya mata, sai ummu adiyya nan take ta nufi wajen manzon Allah (saw) ta gaya masa labarin da `yar'uwarta  ta ba ta, sai ya ce mata matso ya ummu adiyya idan za ki cancadawa mace ado ka da ki wanke fuskarta da kyalle lalle shi kyalle na tafiya da ruwa fuska.

6 – idan an haifi yaro da kaciya mustahabbi ne a shafa aska kan zakarinsa , kamar yadda ya zo a hadisi: daga musa dan jafar (as) ya ce: lokacin da aka haifa ma rida (as) da ya zo da kaciya sai ya ce:  wannan da na wa an haife shi da kaciyarsa da tsarkakakke mai tsarkakewa, sai dai duk da haka zamu goggoga masa aska akan kaciyar don aiki da sunna da bin tafarki miqaqqe.

Sannan daga cikin mustahabbai akwai yin addu'a yayin kaciya:

عن الصادق (عليه السلام) ، في الصبي إذا ختن ، قال  : يقول  : اللهمّ هذه سنّتك وسنّة نبيّك صلواتك عليه وآله ، واتباع لمثالك وكتبك ولنبيّك بمشيّتك وإرادتك وقضائك ، لأمر أردته وقضاء حتّمته وأمر أنفذته ، فأذقته حرّ الحديد في ختانه وحجامته لأمر أنت أعرف به منّا ، اللهمّ فطهّره من الذنوب وزد في عمره وادفع الآفات من بدنه والأوجاع عن جسمه ، وزده من الغنى وادفع عنه الفقر ، فإنّك تعلم ولا نعلم )

7 – an karbo dag sadiq (as) kan yaro idan za'a yi masa kaciya a ce: Allah wannan sunnar k ace da sunnar annabinka amincin Allah ya tabbata gareshi, da kuma da'a ga misalinka da littafinka da annabinka da abin da ka ke so da hukuncinka da iradarka, da al'amarin da ka nufe shi da hukuncin da ka tabbatar da shi da zartar da shi, zan dandana masa zafin qarfe cikin kaciyarsa da qahonsa ga al'amarin da ka ne ma fi saninsa daga gare mu, Allah ka tsarkake shi daga zunubi, ka qara masa tsawon kwana ka ingije masa cutuka  da illoli daga jikinsa, ka qara masa wadata ka ingije masa talauci, lalle kai ka sani mu bamu sani ba.

وعنه (عليه السلام) ، قال  : أيّ رجل لم يقلها على ختان ولده ، فليقلها عليه من قبل أن يحتلم ، فإن قالها كفي حرّ الحديد من قتل أو غيره

8 – imam (as) ya ce: duk mutumin da bai karanta wannan addu'a ba lokacin kaciyar yaronsa ta ya karanta kafin yaron ya balaga, lalle duk wanda ya karanta za 'a ingije masa zafin qarfe daga kisa da makamancinsa.

Kaciya bayan balaga tafi wajabta hatta kan wanda ya muslunta ya zama wajibi ya yi kaciya.

قال أمير المؤمنين (عليه السلام)  : إذا أسلم الرجل اختتن ولو بلغ ثمانين سنة[1]

9 – sarkin muminai ali (as): idan mutum ya muslunta to ya yi kaciya ko da kuwa ya kai shekaru tamanin.

الكافي بسنده عن محمّد بن قزعة ، قال  : قلت لأبي عبد الله (عليه السلام)  : إنّ من قبلنا يقولون  : إنّ إبراهيم ختن نفسه بقدوم على دنّ ـ  قدوم من بلاد الشام  ـ فقال (عليه السلام)  : سبحان الله ليس كما يقولون كذبوا على إبراهيم (عليه السلام) ، قلت  : كيف ذاك  ؟ فقال  : إنّ الأنبياء (عليهم السلام) تسقط عنهم غلفهم مع سُرَرِهم في اليوم السابع فلمّا  ولد لإبراهيم (عليه السلام) من هاجر عيّرت سارة هاجر بما يعيّر به الإماء ـ  ربما عدم خفضهن  ـ فبكت هاجر واشتدّ ذلك عليها ، فلمّا رآها إسماعيل (عليه السلام) تبكي بكى لبكائها ، فدخل إبراهيم (عليه السلام) فقال  : ما يبكيك يا إسماعيل  ؟ فقال  : إنّ سارة عيّرت اُمّي بكذا وكذا فبكت فبكيت لبكائها ، فقام إبراهيم (عليه السلام) إلى مصلاّه فناجى فيه ربّه وسأله أن يلقي ذلك عن هاجر فألقاه الله عنها ، فلمّا ولدت سارة إسحاق وكان اليوم السابع سقطت عن إسحاق سُرّته ولم تسقط عنه غلفته ، فجزعت من ذلك سارة فلمّا دخل إبراهيم (عليه السلام) عليها قالت له  : يا إبراهيم ما هذا الحادث الذي حدث في آل إبراهيم وأولاد الأنبياء  ؟ هذا ابنك إسحاق قد سقطت عنه سرّته ولم تسقط غلفته  ؟ فأوحى الله إليه  : أن يا إبراهيم هذا ما عيّرت سارة هاجر فآليت أن لا اُسقط ذلك عن أحد من أولاد الأنبياء لتعيير سارة هاجر فاختن إسحاق بالحديد وأذقه حرّ الحدى قال  : فختنه إبراهيم بالحديد وجرت السنّة بالختان في أولاد إسحاق بعد ذلك

10 – akafi da isnadinsa daga muhammadu dan qaza'atu, ya ce: na cewa baban Abdullah  (as) lalle wanda suka gabace mu na cewa: Ibrahim (as) ya yiwa kansa kaciya da gatari, sai y ace: subhanallah abin da suke fadi bashi da qamshin  gaskiya lalle sun yiwa ibrahim (as) qarya sai na ce to yaya al'amarin ya kasance? sai ya ce: su annabawa (as) cibinsu da fatar kaciyarsu na faduwa a rana ta bkwai da haihuwarsu yayin da ibrahim ya samu azurtuwa da da daga hajara sai saratu ta yiwa hajara gori da abin da mata kewa kuyangu gori, sai hajara ta fashe da kuka har kukan na ta ya tsananta yayin da isma'il (as) ya ganta ta na sai shi ma take ya fashe da kuka, sai Ibrahim (as) ya shiga ya tambaye shi cewa me ye ya sanya mahaifiyarsa kuka ? sai isma'il

 ya ce: lalle saratu ta yiwa mahaifiyata gori da kaza da kaza to shi ne ta kama kuka ni ma kuka ya kama ni sakamakon kukanta, sai ibrahim ya nufi shimfidar sallarsa yayi munajati da ubangijinsa ya roqe shi da kawar wa da hajara nakasar da ke tare da ita, sai Allah ya cire mata, yayin da saratu ta zo haihuwa sai ta haifi is'haq rana ta bakwai cibinshi ya fadi amma fatar kaciyar ba ta fadi ba, sai saratu ta firgice da ganin wannan al'amari, yayin da Ibrahim (as) ya shiga wajenta sai ta bashi labarin abin ya afku ta ce wannan wanne irin abu ne ya zo ma iyalin ibrahim, ta ce danka is'haq cibinshi ya fadi amma fatar kaciyarsa ba ta fadi ba? sai Allah ya yi wahayi ga ibrahim: ya Ibrahim wanann sakamko ne daga gorin da saratu ta yiwa hajara saboda haka na yi rantsuwa daga yanzu bazan qara cire cibi da kaciya daga kowanne da daga `yayan annabawa ba sakamakon tozarcin da saratu ta yiwa hajara, ka yiwa is'haq kaciya da qarfe ka dandana masa zafinsa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, bayan haka sai wannan sunna ta cigaba cikin `ya`yan is'haq.



[1] Alwafi m 12 sh 1359